Yadda aka kama malamin jami’a akan gado tare da ɗalibarsa

https://apahausa.com.ng/ango-ya-saki-amaryarsa-bayan-an-turo-masa-hotunan-batsarta-a-whatsapp/

An gabatar da malamin jami’ar ‘Kwara University’ mai suna Pelumi Adewole a gaban kotu inda ake zarginsa da neman lalata da ɗaliba.

Malamin ya shiryawa ɗalibar sake rubuta jarabawarta ne a ɗakinsa.

Sai dai tuni ta kaiwa hukuma ƙaransa inda tace ya mata barazanar kayar da ita jarabawa idan bata biya masa buƙatarsa ba.

https://apahausa.com.ng/ango-ya-saki-amaryarsa-bayan-an-turo-masa-hotunan-batsarta-a-whatsapp/

Malamin dai bai daɗe da yin aure ba, inda a watan Yuni da ya gabata ne ya zama ango.

Jami’an tsaro sun gayawa ɗalibar ta bi malamin har inda ya nemeta dan a samu shaida a kansa, inda aka kamashi yana ƙoƙarin lalata da ɗalibar.

Kotu dai ta bayar da belinsa akan naira 200,000 da kuma wani da zai tsaya masa. An ɗaga ƙarar zuwa 8 ga watan Satumba.

Views: 59

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *