LABARI DA DUMI DUMI: Sojojin Najeriya sun kone gaba daya dajin Zamfara

Wata majiya mai karfi daga jihar Zamfara na cewa, sojojin Najeriya sun shafe yini da daren jiya suna ta luguden wuta ta sama da ta kasa a kan sansanin yan bindigar Zamfara inda Rahotanni ke nuna cewa sojojin su kone illahirin dajin baki daya.

Idan ba’a manta ba a farkon makonnan ne gwamnatin Najeriya ta toshe illahirin hanyoyin sadarwa a jihar ta Zamfara, da zummar kawo karshen yan bindigar da suka addabi yankin arewacin Najeriya gaba daya.

Rahotanni dai sun bayyana cewa a halin yanzu babu abinda ya rage cikin dajin sai dai ana kyautata zaton wata kila son gira ramuka sun boye kansu a cikin, wanda a halin yanzu ana ci gaba da bi lungu da sako na dajin domin zakulo su.

Muna fatan Allah ya kara basu nasara a kan wadannan yan ta’adda ameen.

Views: 96

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *