Yadda Ƴan sanda a jihar Kano suka kama jarumar TikTok Murja Ibrahim

Rundunar Ƴan Sandan jihar Kano ta kama fitacciyar mai barkwancin nan ta #TikTok Murja Ibrahim Kunya.

Koda ya ke Ƴan sandan ba su yi ƙarin bayani ba, amma idan zaku iya tunawa a shekarar da ta gabata ne wani lauya ya shigar da ƙorafi inda yake neman da a binciki Murja da wasu fitattun mawaƙa da masu amfani da TikTok kan zargin ɓata tarbiyya.

An kama Murjar ne yayin da take tsaka da shirye-shiryen shagalin bikin murnar zagayowar ranar haihuwarta.

Ƙarin bayani zai zo nan gaba.

Views: 7

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *