Babban Bankin Najeriya wato CBN ya karyata jita-jitar da ake yadawa cewa zata rufe hanyoyin tura kudi na bankuna wato “transfer”
Babban bankin yace bashi da kudurin kawo tsaiku na tura kudi ko karba a lokutan zabe mai zuwa na ranar Asabar.
Tun bayan jita-jitar da ake ta yaɗawa a tsakanin al’umma cewar za’a rufe sabis ɗin tura kuɗi da kiran waya a ranar zaɓen 2023.
Babban Bankin Najeriya wato CBN ya fito ya ƙaryata wannan jita-jitar, inda ya tabbatar da cewa bashi da wani buri na ƙuntatawa mutane da hanasu walwala ranar zaɓe.
source: alfijir hausa
Views: 41
