Yadda Wani Mutum Ya Manta Hanyar Zuwa Garinsu Bayan ya Shafe Shekaru 24 a Gidan Yarin Imo
Sunday Ogbuo, dan asalin UmuochubaAgba, Ekwulobia, a karamar hukumar Aguata ta jihar Anambra, ya manta da hanyar garinsu, bayan ya shafe shekaru da dama a gidan yari na hukumar gyaran hali na Najeriya.
Wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani ya nuna Mista Ogbuo, yayin da wasu mutane ke tattaunawa da shi, inda suka gan shi ya makale a wata mahadar mota a jihar Imo bayan an sako shi daga gidan yari.
A cewar Mr. Ogbuo, ya kasance a gidan yarin jihar Imo tun a shekarar 1999, amma lauyoyin kare hakkin dan Adam sun saka baki an sake shi daga gidan yari a ranar Laraba 14 ga watan Yuni 2023; daga nan sai ya fara neman hanyarsa ta komawa garinsu Ekwulobia a jihar Anambra, kafin wasu Samariya suka gan shi.
A yayin da sukayi hira dashi ya sanar da su cewa ya manta hanayr zuwa garinsu.
Daga Baba Waziri Net
Views: 8
