Ɗa ya ƙone mahaifiyarsa har lahira a jihar Neja

Ɗa ya ƙona mahaifiyarsa har lahira a Naija

Mazauna unguwar Darusalam da ke Minna, Jihar Naija sun tashi cikin kaɗuwa da firgici bayan da wani matashi, mai suna Steven Jiya, ya bankawa mahaifiyarsa, Comfort Jiya wuta.

https://apahausa.com.ng/an-saki-bidiyon-lalatar-mawa%c6%99iyar-najeriya-tiwa-savage/

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa a ranar Litinin ɗin da ta gabata ne dai Steven, wanda ɗan ƙwaya ne, ya dawo da ga garin Suleja a Jihar Naija ɗin dai, inda bayan ya dawo gida ne, sai kawai ta raya masa cewa ya ƙona mahaifiyarsa.

https://apahausa.com.ng/hadiza-da-salamatu-sun-fitar-da-bidiyon-yadda-suke-muala-bayan-sun-auri-junansu/

Jaridar ta ce a lokacin Comfort, wacce tsohuwar Shugabar makarantar sakandire ce, tana tsaka da girki a kicin, sai kawai wannan tambaɗaɗɗen ɗa ya zazzaga mata fetur ya kuma cinna mata wuta a gidanta da ke unguwar Darusalam ya kuma tsere.

https://apahausa.com.ng/hadiza-da-salamatu-sun-fitar-da-bidiyon-yadda-suke-muala-bayan-sun-auri-junansu/

Nan fa ta fito a waje tana ihu a kawo mata ɗauki, inda kan ka ce kwabo, wutar ta ƙone mata ilahirin jikinta.

https://apahausa.com.ng/zan-iya-gamsar-da-maza-biyar-da-jimai-a-lokaci-daya-ba-tare-da-na-gaji-ba/

Wata majiya a dangin marigayiyar ta ce an garzaya da ita asibiti inda ta ke jiyya.

Sai dai kuma, da misalin ƙarfe 3 na yammacin jiya Juma’a, marigayiya Comfort ta ce ga garin ku nan.

Wata majiyar ta ƙara da cewa dama can Steven fitinanne ne kuma ya yi yunƙurin hallaka uwar tun a baya.

Jaridar ta ce ta tuntuɓi rundunar ƴan sanda ta Naija amma haƙar ta ba ta cimma ruwa ba.

Sai dai kuma, in ji jaridar, tuni dai ƴan sandan Caji-ofis na Minna su ka samu nasarar damƙe Steven kuma har an kai shi babbar kotun Minna inda zai girbe abin da ya shuka.

Daily Nigerian Hausa

Views: 30

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *