Budurwar da ta lashe gasar karatun Alkur’ani ta samu kyautar Naira Miliyan 4

Mace ce ta lashe gasar karatun Alkur’ani mai girma a Jihar Zamfara.

Daga Junaidu Ahmadu Doro.

Budurwar da ta zo na Daya a gasar Musabakar karatun Al’kur’ani a jihar Zamfara ta sha Goma ta arziki.

Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni ya Gwangwaje Yarinyar da ta lashe gasar musabakar Al’kur’ani da aka gudanar a jihar Zamfara da abin alkairi.

Ga dai Abubuwan da aka Bata kyauta :

-Na daya an Bata makuden Nairori.


-Na biyu an Bata gida Ginanne a birnin Potiskum na jihar Yobe.


-Na Uku an Bata Aikin yi.


-Na hudu an Bata kujerar aikin Umra ita da mijin da za ta Aura.


-Na biyar an Bata Dama ita da mijin da za ta aura su za6i Jami’ar da su ke so su tafi karatu a duk inda ta ke a fadin Duniya za a biya masu kyauta har su gama karatunsu.

Views: 12

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *