“Ba za mu binne ta ba har sai an dawo da kanta” Iyalin matar da aka sace mata sun yi magana
Iyalan wata tsohuwa ‘yar karamar hukumar Nyeri da aka datse kanta aka kuma sace ta sun tofa albarkacin bakinsu. Iyalin sun ce sun ji takaici saboda ba a kama kowa ba tun bayan kashe danginsu.
An kashe tsohuwa da daddare kuma har ya zuwa yanzu ba a gano kan ta ba. An tsinci gawarta kwance akan gado babu rai a cikin jini. Kofar gidanta ma ta karye. Iyalan sun sha alwashin ba za su binne ta ba har sai an gano kan ta.
Makwabtan sun yi zargin cewa an kashe marigayin ne saboda rashin jituwar fili na iyali da ya rutsa da iyalin. Baya ga wannan rashin jituwar, makwabta sun yi zargin cewa akwai wasu da ke yi wa tsohuwar kaka barazanar ba da filinta. Makwabtan sun ce a shirye suke su yi aiki da ‘yan sanda har sai an samu Adalci.
Makwabtan na zaune cikin fargaba suna cewa wadanda suka kashe tsohuwar za su iya sake kai hari. Allah ya jikan tsohuwar kaka ya huta cikin aminci na har abada.
Source: ke.studio.opera News
From Opera News
Views: 17
