Yadda za’a rage rikicin Manoma da Makiyaya—Miyatti Allah
Shugaban kungiyar Fulani makiyya ta kasa reshen jihar Bauchi Miyetti Allah ta bayyana cewa, dawo da amfani da burtaloli kasar nan ne kawai mafita kan kawo karshen ricikin da ke ci gaba da aukuwa a tsakanin manoma da makiyyan kasar nan.
Shugaban kungiyar reshen jihar Alhaji Sadikue Ibrahim Ahmed a wata hirarsa da manema labarai a jihar Bauchi, inda shugaban ya yi nuni da cewa, batar da burtaloli kasar nan ne Fulani makiyya komawa cikin jeji.
Sadikue ya bayyana cewa, hakan ya jano fulanin makiyaya suke yin kaura zuwa jeji a lokacin rani don su samu su ciyar da dabbobin su.
A cewarsa, amma a yau dabbobin na makiyya sun kasance suna yin kiwo a kan tituna wasu kuma suna kwana a cikin kwangaye.
“Hakan ya jano fulanin makiyaya suke yin kaura zuwa jeji a lokacin rani don su samu su ciyar da dabbobin su.”
Ya sanar da cewa, tun kafin zuwan turawa cikin kasar nan, akwai burtaloli da dabbobin makiyan ke bi, inda ya yi nuni da cewa, hatta wasu guaren da aka kebewa makiyyan wasu mutanen sun yi gine-gine akansu
Shugaban kungiyar ya bayana cewa, sai idan gwamnati ta dawo da burtulolin ne kamar yadda ake da su a jamhuriyya ta biyu a kasar nan, sannan za a samu sa’ida kan yawan samu rikece-rikice a tsakanin makiyya da manoma.
“Tun kafin zuwan turawa cikin kasar nan, akwai burtaloli da dabbobin makiyan ke bi, inda ya yi nuni da cewa, hatta wasu guaren da aka kebewa makiyyan wasu mutanen sun yi gine-gine akansu.”
Ya sanar da cewa, irin cin kashin da ake yiwa makiyya a kasar nan abin takaici ne, inda ya kara da cewa, da yawan su an kore su daga guraren da kakaknsu suke tun asali kusan sama da shakaru 100. duk shekara, ana yawan samu rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani makiyya a kasar nan.
Views: 14
