HOTUNA: “Yadda wata Akuya ta Haifi rabi Mutum rabi Dabba a Jihar Kwara

HOTUNA: “Yadda wata Akuya ta Haifi rabi Mutum rabi Dabba a Jihar Kwara

Wani abin mamaki ya faru a wani ƙauye da ke jihar Kwara, inda akuya ta haifi ɗa mai siffar mutane.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Adigun-Oke da ke ƙaramar hukumar Ifelodun ta jihar KwaraMutane da dama sun yi tururuwa zuwa ƙauyen domin ganewa idanunsu wannan abin al’ajabi.

Kwara – Wata akuya ta haifi ɗanɗa wanda wani ɓangare na jikinsa na mutum ne, yayin da wani ɓangaren kuma na akuya a ƙauyen Adigun-Oke, da ke ƙaramar hukumar Ifelodun ta jihar Kwara.

Wannan abin mamaki wanda ya ja hankulan jama’a ya faru ne a ranar Laraba ta makon da ya gabata kamar yadda jaridar Nigerian Tribune ta wallafa.Akuya ta haifi rabi mutum rabi akuyaAishat Umar, wacce mijinta ne ke da akuyar, ta bayyana cewa ‘ya’ya biyu ne ta haifa, inda ɗaya daga cikinsu ya zo da halittu irin na ɗan adam baya ga kunnuwansa da kafafunsa.Wani daga cikin shugabannin al’umma na yankin mai suna Pa James Adeoye, ya bayyana cewa sun ga mutane suna ta tururuwa zuwan gidan da lamarin ya faru, inda suka je suka tarar da wannan abin mamaki.

Ya ce ɗaya daga cikin ‘ya’yan da akuyar ta haifa jikinsa rufe yake da gashi irin na akuya, sai dai shi kuma ɗayan yana ɗauki da kamanni irin na mutane kamar yadda The Nation ta wallafa.

Views: 19

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *