Kotun Shari’ar Muslunci a jihar Kano ta aike da Murja Ibrahim zuwa gidan yari

Kotu ta aike da Murja Kunya zuwa gidan yari

Kotun shari’ar Muslunci da ke Filin Hoki a Kano ƙarƙashin mai Shari’a Abdullahi Halliru ta aike da Ƴar TikTok ɗin nan Murja Ibrahim Kunya zuwa gidan yari.

https://apahausa.com.ng/video-ku-kalli-yadda-%c6%b4a%c6%b4an-hausawa-suka-lalace-zina-a-fili/

Lauya Barrister Lamiɗo Abba Soron Ɗinki ya karanto mata ƙunshin tuhume-tuhumen da ake mata wanda ta musanta.

Ana zargin Murja da ɓata suna da barazana ga Aisha Najamu ta Izzar So da kuma Ashiru Idris wanda dukanninsu abokananta ne.

https://apahausa.com.ng/video-ku-kalli-yadda-%c6%b4an-bindiga-ke-lalata-ta-matan-mutane/

Kotun ta ɗage sauraron ƙarar zuwa 16 ga watan Fabrairun da muke ciki.

Sai dai Lauyan Murja Barrister Yasir Musa ya nemi a tura ta zuwa Hisbah maimakon gidan Yari sai dai Kotun bata amince ba.

Views: 25

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *