“Yadda ake samun kuɗi ta internet Najeriya”
Yadda ake samun kuɗi ta internet a Najeriya ya zama ɗaya daga cikin hanyoyin samun kuɗin shiga da suka fi shahara a shekarar 2026. A wannan jagorar, za ka koyi hanyoyi masu sauƙi da ingantattu da za su taimaka maka fara samun kuɗi online cikin halal.
Yadda ake samun kudi ta internet Najeriya a cikin 2026
Akwai hanyoyin samun kuɗi ta Internet masu yawa sai wanda mutum ya zaɓa duk da cewar akwai na ƙarya akwai ma na damfara amma yau insha Allahu zan nuna muku hanyoyi kamar guda 3 da suke ingantattu.
Idan Facebook suka buɗe maka hanyar samun kuɗi ta subscription, ga yadda zakayi:
https://apahausa.com.ng/yadda-ake-samun-kudi-ta-internet-a-najeriya
- Kayi accepting
- Kayi setting payment information ɗinka (account number)
- Kayi selecting adadin kuɗin da mutane zasu biya kowane wata domin ganin postings ɗinka (N350 N500 N1000 N2000 N5000)
Bayan haka
Idan kaje yin posting, wurin da ake saita audience zakayi selecting (subscribers) a maimakon (friends, public, ko followers)
Idan kayi wannan, sai wanda suka yi subscription ɗin page ɗinka zasu ga wannan posting
⚠️ ilimi mai muhimmanci shine yadace ayi subscribing
Kamar irin koyarda mutane hanyoyin samun kudi a yanar gizo, crypto, gyaran waya, ilimin kiwon lafiya, ilimin addini, da darussa masu muhimmanci wanda zasu amfane al’umma.
Ga Tambaya misali ga Adsterra zaka iya samun kudi dasu cikin sauki
https://beta.publishers.adsterra.com/stats
KA TAƁA FADAWA CIKIN ASARAR CRYPTO?
Daga Eng Muhammad Sunusi — Head of Media & Communications
NovaChain Blockchain Academy.
Yaushe za ka daina nadamar abin da ya faru da kai a duniyar Crypto? Yaushe za ka daina cewa, an cuce ni? Gaskiyar magana ita ce, rashin ingantaccen ilimi na daga cikin manyan dalilan da ke jefa mutane cikin matsaloli a wannan fage. Shi yasa aka kafa NOVACHAIN BLOCKCHAIN ACADEMY, domin taimaka maka ka fahimci Blockchain da Crypto daga tushe, cikin tsari mai kyau kuma a harshen Hausa.
A NovaChain, ba saka jari ko Mining zamu koya maka ba. Za mu taimaka maka ka fahimci ainihin yadda Blockchain da Crypto suke aiki, damammakin da ke cikinsu, da kuma ƙwarewar da zaka iya amfani da ita a wannan sabuwar duniyar fasaha. Zaku koyi yadda zaku gano da kuma nemowa kanku damammaki a duniyar Blockchain, ta hanyar ilimi da ƙwarewa, koda bakuda jarin ko kwabo.
Koda baka da wani ilimi game da Blockchain ko Crypto, ko kuma kana da ɗan ilimi kuma kana son ƙara zurfafa fahimtarka, akwai gurbin ka a NovaChain Blockchain Academy. Kana son sanin tsare tsaren wannan Academy? Ka ziyarci Telegram Channel ɗinmu domin samun cikakken bayani da kuma bibiyar duk abubuwan da ke gudana:
Muna maraba da zuwanku NOVACHAIN BLOCKCHAIN ACADEMY Inda Ilimi Ya Zama Farkon Tafiya.
A wani labarin kuma
Rundunar yaƙi da masu ƙwacen waya ta Kano ta kama matashi kan zargin tayar da tarzoma
Rundunar yaƙi da masu ƙwacen waya ta Jihar Kano (Anti-Phone Snatching Force) ta ce ta kama wani matashi da aka fi sani da Suda bisa zarginsa da hannu a faɗace-faɗacen daba da suka shafi wasu sassan Unguwar Kuntau zuwa Dorayi Babba.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Mustapha Sunusi Mu’azu, ya fitar, ya ce an kama wanda ake zargin ne yayin wani samame da jami’an tsaro suka gudanar.
Sanarwar ta ce ana zargin matashin da haddasa tarzoma da kuma tayar da hankalin jama’a a wasu yankuna, lamarin da ta ce ya janyo rashin zaman lafiya.
Rundunar ta ƙara da cewa ana ci gaba da bincike domin tantance rawar da wanda ake zargin ya taka tare da gano ko akwai wasu da ake zargin suna da hannu a lamarin.
Kazalika, Kwamandan rundunar, Nura Salisu Sharada, ya yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai kan duk wani abu da ka iya zama barazana ga tsaro, domin taimaka wa ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya.
Tinubu ya yi kira ga ECOWAS ta ɗauki tsauraran matakai kan Afirka ta Kudu kan batun hare-haren ƙyamar baƙi
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci ƙasashen da ke ƙarƙashin Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) su haɗa kai wajen yin Allah wadai da sabbin hare-haren ƙyamar baƙi da ake kai wa ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka a ƙasar Afirka ta Kudu. Ya ce dole ne ECOWAS ta gabatar da batun a gaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) domin ɗaukar matakin gaggawa kan lamarin.
Tinubu ya bayyana wannan matsaya ne ta bakin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, yayin taron shugabannin ECOWAS karo na 69 da aka gudanar a Freetown na ƙasar Saliyo. A cewarsa, gwamnatin Najeriya ta yi Allah wadai da hare-haren tare da bayyana cewa shirun diflomasiyya kan irin waɗannan abubuwa na ƙarfafa masu aikata su. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kwashe fiye da ‘yan Najeriya 1,490 daga Afirka ta Kudu cikin jigilar jirage bakwai domin kare rayukansu.
Rahotanni sun nuna cewa Najeriya na ƙoƙarin haɗa kai da Ghana domin matsa wa AU lamba ta hukunta Afirka ta Kudu kan ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi. Ana ganin lamarin ba ‘yan Najeriya kaɗai ya shafa ba, har da dubban ‘yan ƙasashen Afirka da ke zaune da aiki a Afirka ta Kudu, waɗanda su ma ke fuskantar irin wannan barazana.
Baya ga batun hare-haren, Tinubu ya sake jaddada aniyar Najeriya na goyon bayan ECOWAS Compact for the Future of Regional Integration, shirin da ke da nufin ƙarfafa haɗin kan ƙasashen yankin, inganta shugabanci nagari, bunƙasa kasuwanci tsakanin ƙasashe da samar da kasuwar hada-hada ta yanar gizo guda ɗaya domin ƙara samar wa matasa ayyukan yi. Ya ce tabbatar da shugabanci nagari da kare rayukan ‘yan Afirka su ne ginshiƙan ci gaban nahiyar.
Views: 4
