
Kamar yadda shafin yaɗa labarai na HausaLoaded ya ruwaito.
Yadda Maryam Abubakar Matar Aure Ke Kwanciya Da Ɗan Bindiga, Sannan Takai Musu Wasu Matan Zuwa Cikin Daji Tare Sauran Ababen More Rayuwa.
A cikin shekara ta 2021 kadai, yan bindiga da ke ayyukan ta’addanci a sassa daban-daban na Arewacin Najeriya musamman a yankin Arewa maso Yamma, sun kashe gomman mutane, tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin Naira.
Ƴan bindigar sun kuma yi awon gaba da yara ‘yan makaranta da yawa, tare da neman kudin fansa domin sako su.
Ƴan bindigar sun kuma mayar da yankin ya zama wuri mafi rashin tsaro a kasar. Abin baƙin ciki, duk da haka, wasu matan da ya kamata su fahimci irin barnar da ƴan bindigar ke yi musamman yadda ayyuka ƴan bindigar suka shafi mata da yara, haka wasu matan irin su Maryam suka rufe ido suka cigaba da yi wa ƙungiyoyin masu ɗauke da makaman aiki.
Views: 29
