DSS suka mamaye gidan yarin Kirikiri da ke Legas

Hankali yatashi yayin da DSS suka mamaye gidan yarin Kirikiri da ke Legas bayan ‘barazana’ ga rayuwar diyar Osinbajo

Akwai fargaba yayin da jami’an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) suka kai farmaki gidan yarin Kirikiri Maximum Security dake jihar Legas.

A cewar Daily Post, ma’aikatan da aka ce sun haura goma sha biyu, sun isa gidan yarin da ke unguwar Apapa da yammacin ranar Lahadi, 12 ga Maris, 2023.

Kasancewarsu na da nasaba da yunkurin kashe daya daga cikin ‘ya’yan mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo.

An tattaro cewa wanda aka kai harin, wanda ake zargin fursuna ne, ya yi amfani da wayar salula wanda jami’an sirrin suka bi diddigin inda suke.

“Hukumar DSS na can tun ranar Lahadi da yamma, kuma ba shakka kasancewarsu ya haifar da fargaba.

“Jami’an sun yi imanin cewa mutumin da suke nema yana cikin daya daga cikin sel ko kuma wani wuri kusa da gidan yarin,” wata majiya ta bayyana.

Jami’in Hulda da Jama’a na DSS, Peter Afunanya ya bukaci a aika masa sakon tes lokacin da aka tuntube shi domin jin ta bakinsa. Babu amsa har zuwa lokacin da aka buga labarin.

Views: 24

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *