Rikici ya ɓarke a Burkina Faso bayan sojoji sun kifar da gwamnatin Kabore

Wasu dakarun ƙasar ta Afirka ta Yamma sun nemi a kori wasu manyan jami’an soja da kuma samar da ƙarin kayan aiki don yaƙar masu iƙirarin jihadi.

An jiyo harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasa da kuma wasu barikin soja ranar Lahadi da dare a Ouagadougou babban birnin ƙasar.

Sai dai gwamnati ta musanta labarin yunƙurin juyin mulki ko kuma cewa an kama shugaban ƙasar .

Rahotanni na cewa ana tsare da Shugaba Kabore ne a wani sansanin soja.

Kazalika, sojoji sun kewaye gidan talabijin na gwamnatin ƙasar.

Ɗaruruwan mutane ne suka fito zanga-zangar nuna goyon baya ga sojojin duk da dokar hana fita da aka saka, sannan suka dinga ƙona ofisoshin jam’iyya mai mulki.

Bidiyon da aka rika yadawa a babban birnin kasar ya nuna wasu motoci masu sulke – wadanda rahotanni suka ce na fadar shugaban kasa ne – dauke da harbe-harben bindiga kuma an bar su a kan toituna.

Wakilin BBC Simon Gongo da ke Ouagadougou ya ce birnin ya yi tsit. Sai dai sojoji sun kewaye gidan talbijin na kasar.

Views: 20

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *