Rikici ya ɓarke a Burkina Faso bayan sojoji sun kifar da gwamnatin Kabore

Wasu dakarun ƙasar ta Afirka ta Yamma sun nemi a kori wasu manyan jami’an soja da kuma samar da ƙarin kayan aiki don yaƙar masu iƙirarin jihadi.

https://apahausa.com.ng/an-saki-bidiyon-lalatar-mawa%c6%99iyar-najeriya-tiwa-savage/

An jiyo harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasa da kuma wasu barikin soja ranar Lahadi da dare a Ouagadougou babban birnin ƙasar.

https://apahausa.com.ng/an-kama-%c9%97a-da-uba-suna-yiwa-%c6%b4ar-shekara-13-fya%c9%97e-a-jihar-osun/

Sai dai gwamnati ta musanta labarin yunƙurin juyin mulki ko kuma cewa an kama shugaban ƙasar .

Rahotanni na cewa ana tsare da Shugaba Kabore ne a wani sansanin soja.

https://apahausa.com.ng/labari-da-dumi-dumi-miji-ya-kama-matarsa-na-turawa-tsohon-saurayinta-bidiyon-ta-tsirara-a-whatsapp/

Kazalika, sojoji sun kewaye gidan talabijin na gwamnatin ƙasar.

Ɗaruruwan mutane ne suka fito zanga-zangar nuna goyon baya ga sojojin duk da dokar hana fita da aka saka, sannan suka dinga ƙona ofisoshin jam’iyya mai mulki.

https://apahausa.com.ng/labari-da-%c9%97umi-%c9%97umi-sadiya-haruna-ta-saki-bidiyon-lalatar-da-aka-yi-da-wata-%c6%b4ar-film/

Bidiyon da aka rika yadawa a babban birnin kasar ya nuna wasu motoci masu sulke – wadanda rahotanni suka ce na fadar shugaban kasa ne – dauke da harbe-harben bindiga kuma an bar su a kan toituna.

Wakilin BBC Simon Gongo da ke Ouagadougou ya ce birnin ya yi tsit. Sai dai sojoji sun kewaye gidan talbijin na kasar.

Views: 54

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *