Tsohon Gwamnan Kano ya umarci masoyansa su kauracewa shafukan Sahara Report

Wani magoyin bayan tsohon gwamnan jihar Kano kuma tsohon sanatan shiyyar Kano ta tsakiya a majalissar dattawan tarayyar Najeriya wato Engr. Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya umarci duk wani mai goyon bayan jagoransa.

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da kungiyarsu ta Kwankwasiyya, akan ya kauracewa bibiyar shafukan yanar gizo na jaridar Sahara Report sakamakon wani rubutu da jaridar tayi a ranar litinin wanda ya taba martaba da kimar MANZON ALLAH SAW.

Mutumin mai suna Umar Kwankwason Dala yace da yawun jagora yake wannan magana saboda haka don Allah duk wani dan Kwankwasiyya na kwarai ya bi wannan umurni na kauracewara illahirin shafukan Saharar gaba daya.

Views: 13

One thought on “Tsohon Gwamnan Kano ya umarci masoyansa su kauracewa shafukan Sahara Report

Leave a Reply to Muhammad khamis Abubakar Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *