Bana Iya bacci ko tafiya, saboda harsashin da ke yawo a cikina – Matar Sheikh Zakzaky.

Uwargidan jagoran Harkar Musulunci a Najeriya (IMN) wato Zeenah El-Zakzaky ta koka da irin radadin da take ji na halin da ta shiga sakamakon harsasan da ke yawo a cikin ta na harbi da Sojojin tsohuwar Gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari suka yi mata a Zariya.”
An harbe ta ne tare da mijinta, Sheik Ibraheem El-Zakzaky a Zariya, jihar Kaduna a ranar 14 ga Disambar shekerar 2015, inda Sojojin suka kwashe tsawon kwanaki biyu suna luguden wuta kan daruruwan mabiya Shi’a.
Sama da gawarwakin mutane 300 ne sojoji suka binne a asirce a wani kabari, a cewar hukumar kare hakkin dan adam ta Human Rights Watch.
A halin yanzu Zeenah ta ce tana fama da mugun ciwon ciki wanda ya hana ta komai.
Ta bayyana hakan ne a ranar Asabar din da ta gabata a yayin taron ranar Qudus a birnin Abuja.”
Views: 8
