Ina kira ga Kotu ta yankewa makashin Hanifa hukuncin rataya a bainar jama’a—Aisha Buhari

Uwar Gidan shugaban Ƙasa A’isha Buhari Tayi Kira Da a Rataye Wanda Ya Kashe Hanifa a Bainar Jama’a.

Cikin wani bidiyo na Malam Abdallah Gadon Ƙaya da yake cewa; ya kamata a kashe Abdulmalik, uwargidan shugaban ƙasa, Hajiya A’isha Buhari ta goyi bayansa inda ta saka bidiyon a shafinta na sada zumunta tace muna tare da Malam.

Abdulmalik Tanko dai wanda shine shugaban makarantar Noble kids Academy dake Kawaji a Nasarawa dake Kano, ya amsa cewa shine ya kashe Hanifa.

Inda ya bayyana cewar, yayi amfani da maganin Ɓera ne wajan kisanta, tare da sanya gawarta cikin buhu ya binneta.

©Idonmikiya

Views: 21

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *