Majalisar ɗinkin Duniya ta dakatar da aikin agaji a Jamhuriyar Nijar

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce ta dakatar da dukkan wasu ayyukan agaji a Nijar, kwana biyu bayan sojoji sun sanar da juyin mulki a ƙasar.

Ta ce a yanzu haka akwai mutum fiye da miliyan hudu da ke matuƙar bukatar agaji a Nijar din.

Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniyar Antonio Guterres ya buƙaci sakin shugaban ƙasar Mohammed Bazoum wanda ke tsare a wajen sojojin ba tare da ɓata lokaci ba.

Shima ministan harkokin wajen Faransa ya ce shugaba Bazoum ɗin ya tattauna da shugaba Emmanuel Macron a safiyar yau kuma ya ce ana iya magana da shi sannan yana cikin koshin lafiya.

source: bbc hausa

Views: 37

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *