Zamu mayar da gidajen kallo makarantun Islamiyya—Gov Masari

Hoto Daga DW

Gwamnatin jihar Katsina a kar kashin jagorancin mai girma gwamna Aminu Bello Masari, ta sanar da cewa za ta mayar da gidajen kallo makarantun islamiyya a fadin jihar.

Wani dan majalissar dokokin jihar ta Katsina ne dai ya gabatar da wannan kuduri a zauren majalissar dokokin jihar, bayan majalissar ta duba sannan ta tabbatar da zar tas da kudurin kafin daga bisani gwamnan jihar ya sa hannu a kan kudurin.

Hukuncin dai zai shafi gidajen kallon da gwamnatin jihar ta gina domin haska wasanni, daga yanzu za’a rufe su a daina kallo kwata kwata, inda a mai makon haka za’a rika koyar da yara karatun islamiyya.

Views: 26

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *