Babban limamin babban masallacin Suleja a jihar Neja, Sheikh Dahiru Shuaibu, ya riga mu gidan gaskiya ranar Asabar, 22 ga watan Yuli ƴan sa’o’i kaɗan bayan ya dawo daga aikin Hajji a ƙasa mai tsarki.
Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa wani daga cikin iyalan mamacin, Abduljalil Dahiru Shuaibu, ya bayyana cewa limamin wanda ya dawo Saudiyya ranar Asabar da misalin ƙarfe 9:00 na safe, ya rasu ne sakamakon bugun zuciya da misalin ƙarfe 11:00 na dare a gidansa.
Views: 12
