
Rahotannin da ke shigo mana da dumi duminsu yanzu na cewa sojojin Najeriya, na can suna ci gaba da luguden wuta ta sama da ta kasa a kan sansanin yan bindiga masu tada kayar baya.
Hare haren na zuwa ne bayan shafe daren jiya suka kai musu hare hare ta sama da ta kasa a cikin dajukan da suka boye, yanzu haka dai rahotanni na cewa jami’an tsaron sun kusan kune kashi 40 na illahirin dajin.
Ko a jiya ma sashin hausa na BBC ya bada rahoton cewa,
Wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar Zamfara Ibrahim Dosara ya fitar ta ce sansanonin da aka tarwatsa a hare-haren sojin saman Najeriya sun haɗa da wani ƙasurgumin ɗan fashin daji da ake kira Dan ƙarami a ƙaramar hukumar shinkafi
A cewar sanarwar a baya ɗan fashin dajin ya fitar da wani bidiyo yana murna bayan artabun da suka yi da sojoji.
Views: 155
